![Addu'ar da Yadace Manoman FMARD, AFJP Farmers Suyi A Kowace Safiya Addu'ar da Yadace Manoman FMARD, AFJP Farmers Suyi A Kowace Safiya](https://blogger.googleusercontent.com/img/b/R29vZ2xl/AVvXsEgDYUae9OOkep3PcoZa-kRwgNTPPQUuNWilGWBKIwsf_w14_zy17JlLPckpTle5aa3opnbvmcfaoLdudsxJAIYjziyBg82it3-VGFXOFzdbuFuglMPyxydoh0gys6jQ-JmVsLJcd_F_7W0/s16000/IMG_20210711_235216.jpg)
Addu'ar da Yadace Manoman FMARD, AFJP Farmers Suyi A Kowace Safiya
Addu'ar da Yadace Manoman FMARD, AFJP Farmers Suyi A Kowace Safiya
_*TAMBAYA.*_
Assalamu alaikum.. Dan Allah Malam. Wani adduane Mutun zaiyi idan yana rokan Allah yabashi wani abu?
_*AMSA:*_
_Wa'alaikumussalamu Warahmatullah._
_Yana da kyau me addu'a Ya kaskantar da kansa ga Ubangiji, sannan ya cire kokonton amsar addu'ar a zuciyarsa._
_An karbo hadisi daga Buraidata (r.a) ya ce: *manzon Allah (ﷺ)* ya ji wani mutum yana cewa: *Allahumma inni as'aluka bi anni ash-hadu annaKa antallahu Laa ilaaha illa anta, al-ahadus samadu, alladzi lam yalid wa lam yulad wa lam yakun lahu kufwan ahad,* sai manzon Allah (ﷺ) ya ce: *“Lallai ka yi roƙo da sunan da Idan aka yi roƙo da shi ana bayarwa, kuma idan aka yi addu'a da shi ana amsawa".* mutane hudu suka ruwaito shi, Ibn Hibban ya inganta shi._
_Wannan hadisin na nuna mana kenan ana saurin amsa addu'ar Wanda ya yi amfani da wadannan 👆🏾sunayen kenan._
_Saboda haka 'yar uwa Idan za ki yi addu'a, sai ki fara ambaton wadancan sunayen, sannan sai addu'ar ta biyo baya._
Wallahu A'alamu
0 Response to "Addu'ar da Yadace Manoman FMARD, AFJP Farmers Suyi A Kowace Safiya"
Post a Comment